9 Mayu 2021 - 14:04
Mali: Wata Mata Ta Haifi ‘Ya’ya 9 A Lokaci Guda

Wata mata a kasar Mali ta haifi ‘ya’ya 9 a lokaci guda, haihuwa irinta na farko a kasar. Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayyana cewa matar mai suna Halima Cisse ta haifi yayan na ta ne a kasar Morocco bayan da lokitoci a kasar Mali suka ga tana bukatar kula na musamman bayan sun gano cewa tana dauke da cikin yara 7. Amma bayan haihuwarta a kasar Mrocco an gano tana dauke da yara har tara.

ABNA24 : Yara 5 mata 4 maza, tare da mahaifiyansu duk suna cikin koshin lafiya, inji ministan lafiya na kasar Mali Fanta Siby. Daga karshe ministan ta ce dukkan haihuwar tiyata ce, bata haihu da kanta ba. Ba’a cika samun haihuwar yara 9 a lokaci guda a cikin mutane ba.

342/